Ranar 31 ga watan Yuli za a gudanar da zaben shugaban kasa a Zimbabwe
Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, ya yi alkawalin gudanar da zaben shugabancin kasar na ranar 31 ga wannan wata a cikin kyakkyawan tsari, sannan kuma a cikin kwanciyar hankali ba kamar yadda kasashen yamma ke zargi ba.
Wallafawa ranar:
Mugabe wanda ke gabatar da jawabi a gaban magoya bayan sa fiye da dubu 40 a filin kwallon kafa na kasar da ke Harare, ya ce ba ya da niyyar tislata wa wani ko wata jefa kuri’arsu ga dan takarar da ba sa bukata.
Ana sa ran da dama daga cikin yan kasar ne za su futowa ranar 31 ga watan yuli na shekara 2013 domin bayyana zabin su tsakani firaminista Morgan Tsvangirai da Shugaban kasar Robert Mugabe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu