Isa ga babban shafi
Masar

Jami'an tsaron Masar na kokarin kama 'yan Jama'iyyar 'yan uwa Musulmi

Wata sabuwar takaddama ta barke a Masar yayin da jami’an tsaro ke yunkurin cafke wasu magoya bayan jama’iyyar ‘yan uwa musulmi da hambararren shugaban kasar, Mohammed Morsi, wadanda suke boye a wani masallaci dake birnin Alkahira. Wannan lamari na zuwa ne a dai dai lokacin da magoya bayan hambararren shugaban, ke shirin gudanar sabbin zanga zanga a sassa daban daban na kasar.Ko a jiya juma’a, akalla mutane 80 ne suka mutu a wata arangama da aka yi tsakanin bangarorin biyu, lamarin da har ila yau ya yi sanadiyar cafke magoya bayan Morsi su sama da 1000. 

Magoya bayan hambararren shugaban Masar, Mohamed Morsi
Magoya bayan hambararren shugaban Masar, Mohamed Morsi REUTERS/Louafi Larbi
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.