Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Compaore na sa ran sake tsayawa takara a 2015.

An gudanar da bukukuwan cikon shekaru 53 da samun yanci  a garin Dori dake  kasar  Burkina  Faso  cikin halin rashi sani tabas dangane da  makomar  kasar a  shekara ta 2015,yayi da yan siyasa ke ciggaba da bayana  korafin su ga abinda suka kira  yiwa  dimokradiya targade  da Shugaban kasar Blaise Compaore  ke shirin aikatawa.

Shugaban Burkina Faso, Blaise Compaoré.
Shugaban Burkina Faso, Blaise Compaoré. REUTERS/Noor Khamis
Talla

Shugaban kasar Burkina Faso Balise Conpaore a jiya alhamis ya bayyana aniyar sa na kiran zaben raba gardama a kasar, domin kawo gyaran fuska ga ayar doka mai lamba 37 dake kumshe  cikin kundin tsarin mulkin kasar, da ta kayyade wa’adin shugabancin kasar sau biyu ba kari, domin samun damar sake tsaya takara a jere a shekara ta 2015.

Blaise Compaore,Shugaban kasar  Burkina  Faso  ya hau madafin ikon  kasar ne tun a  shekara ta 1987,bayan wani juyin  mulkin da yayi sanadiyar mutuwar tsohon Shugaban  sojin  kasar  Thomas Sankara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.