Isa ga babban shafi

'Yan uwa Musulmi sun yi watsi da matakin Gwamnatin Masar

Jam’iyyar ‘yan uwa musulmi ta kasar Masar ta yi watsi da matakin hukumomin kasar da suka bayyana ta a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda tare da haramta wa magoya bayanta damar shirya zanga-zanga ko kuma taron gangami.

Babban hafsan Sojin kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi
Babban hafsan Sojin kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi REUTERS
Talla

Gwamnatin Masar ta dauki wannan matakin ne bayan wani hari da aka kai a ginin ‘Yan sanda a birnin al Kahira.

Amma Daya daga cikin manyan jami’ai a jam’iyyar ‘Yan uwa musulmi mai suna Ibrahim Munir da ke guddun hijira a birnin London, yace duk da wannan mataki na gwamnati, magoya bayansu za su ci gaba da tarzoma har sai an mutunta zabin jama’a a kasar.

Wannan matakin zai kara hura wutar rikicin kasar Masar inda darururwan mutane suka mutu tun lokacin da sojoji suka hambarar da gwamnatin Morsi a watan Yuli wanda shi nene shugaban Dimokuradiya na farko a Masar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.