Somalia: Mutane 7 sun mutu a harin al Shebab
Mayakan Kungiyar al Shebab sun dauki alhakin kai harin bom a cikin wata mota da ya kashe mutane 7 a birnin Mogadishu a yau Alhamis. Kungiyar dai ta kai harin ne a kusa da hedikwatar Jami’an tsaro.
Wallafawa ranar:
Kungiyar al Shebab ta dade tana kai hare hare a gine ginen gwamnati saboda adawa da shugabannin kasar da ke samun goyon bayan kasashen yammaci.
Kakakin kungiyar Abdul'aziz Abu Musab ya tabbatarwa Kamfanin Dillacin Labaran Faransa cewa su suka kai hari a Mogadishu domin karyata ikirarin gwamnati game da samun nasara akansu.
Rahotanni dai sun ce bom din ya tashi ne tare da wani da ke tukin motar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu