‘Yan bindiga sun kashe Sojojin Algeria 11
Wasu ‘Yan bindiga sun kai wa Sojojin Algeria harin kwantar bauna inda suka kashe Sojoji 11 tare da raunata wasu da dama kamar yadda rundunar sojin kasar ta tabbatar, wannan kuma shi ne hari na farko da aka kai bayan Shugaban kasa Abdelaziz Boutefilika ya lashe zabe wa’adi na hudu.
Wallafawa ranar:
Ma’aikatar tsaron kasar tace harin ya faru ne a yankin Kabylie mai fama da rikici wanda ke gabas da garin Algiers.
Sanarwar ma'aikatar tsaron kasar tace, an abkawa tawagar sojojin ne lokacin da suke dawo wa daga wani aiki. Yanzu haka sojoji sun ce suna farautar wadanda suka aikata kisan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu