Isa ga babban shafi
Najeriya

Goodluck Jonathan a Chibok

Ana sa ran Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan zai kai ziyara a garin Chibok inda Mayakan Boko Haram suka sace ‘Yan mata sama da 200, kuma ziyarar Shugaban na zuwa ne fiye da wata guda da aka yi awon gaba da daliban 'Yan Makarantar Sakandare.

Wata 'Yar Makaranta tana nuna abokiyar karatunta cikin 'Yan matan da Mayakan Boko Haram suka sace a Chibok
Wata 'Yar Makaranta tana nuna abokiyar karatunta cikin 'Yan matan da Mayakan Boko Haram suka sace a Chibok REUTERS/Stringer
Talla

Wani babban Jami’in gwamnatin Jonathan ya shaidawa Kamfanin Dillacin Labaran Faransa cewa shugaban zai kai ziyara Jahar Borno kafin ya nufi birnin Paris na Faransa don halartar taron tattauna tsaron yammacin Afrika da barazanar Boko Haram.

Ziyarar Jonathan a Chibok na zuwa ne a yayin da ya ke fuskantar suka da matsin lamba daga ‘Yan Najeriya da kasashen duniya akan tafiyar hawainiya da gwamnatinsa ke yi wajen kubutar da ‘yan matan da aka sace a ranar 14 ga watan Afrilu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.