Isa ga babban shafi
Ghana

Ebola: Ministocin Lafiya na Yammacin Afrika suna taro a Ghana

Ministocin lafiya daga kasashen yammancin Afrika suna gudanar da taro a kasar Ghana domin tattauna hanyoyin dakile yaduwar cutar Ebola da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama a kasashen Guinea da Liberia da Saliyo.

Likitoci suna gwajin kwayoyin cutar Ebola da ta barke a kasashen Afrika
Likitoci suna gwajin kwayoyin cutar Ebola da ta barke a kasashen Afrika AFP/Cellou Binani
Talla

Wannan matakin dai na zuwa ne bayan da aka ci gaba da samun sabbin mutane da ke kamuwa da cutar da kuma yadda cutar ke jefa rayuwar ma’aikatan lafiya cikin hadari

Abdousalam Nasidi wanda ya wakilci Ministan Lafiya a Najeriya ya shaida RFI Hausa cewa zasu tattauna hanyoyin dakile yaduwar cutar a yankin Afrika ta yamma saboda yadda cutar yaduwar a cikin hanzari.

Tuni Majalisar Dinkin Duniya ta yi alkawalin zata taimaka a shawo kan cutar.

Hukumar Lafiya ta duniya WHO tace kimanin mutane 467 suka mutu, tare da yin gargadin adadin na iya karuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.