Isa ga babban shafi
Faransa-Afrika

Faransa zata baza dakaru a Sahel

Gwamnatin Faransa tace Sojojinta da suka kwato arewacin Mali zata baza su a Sahel domin dakile ayyukan ta’addanci a yankin, kamar yadda Ministan tsaro Jean-Yves Le Drian ya tabbatar a wata tattaunawa a kafar Telebijin.

Wani Sojan Mali a yankin Kidal.
Wani Sojan Mali a yankin Kidal. (Photo : AFP)
Talla

A watan Janairun bara ne Faransa ta aika da dakaru domin taimakawa Sojojin Mali kwato yankin arewaci da ya fada ikon ‘Yan tawayen Abzinawa da Mayakan MUJAO.

Ministan tsaron Faransa yace nan ba da jimawa ba ne Sojojin zasu kaddamar da yaki a Sahel tare da hadin gwiwar kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar da Chadi da Mauritiania.

Le Drian yace kimanin Sojojin Faransa 3,000 ne zasu yi aiki a yankin Sahel, yayin da Sojoji 1,000 za su ci gaba da kula da sha’anin tsaro a Mali.

Sojojin kuma zasu yi amfani da manyan jiragen sama da kanana da wadanda ke tuka kansu da tankokin yaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.