Wani Jirgin Algeria ya bata
Kamfanin Jiragen sama na Air Algerie yace wani jirginsa dauke da fasinja 110 ya bata bayan ya tashi daga Ouagadougou kasar Burkina Faso zuwa birnin Algiers. Kamfanin yace bayan tashin jirgin da misalin awa daya ba a sake jin duriyarsa ba.
Wallafawa ranar:
Wata Majiyar Kamfanin ta shaidawa Kamfanin Dillacin labaran Faransa cewa jirgin ya bata ne a lokacin da ya doshi kan iyakar Algeria daga sararin samaniyar kasar Mali.
Majiyar tace Jirgin na iya yin karo da wani Jirgi idan har ba ji duriyarsa ba.
A watan Fabrairu wani Jirgin Soji na Algeria ya taba yin hadari inda mutane 70 da ke cikinsa suka mutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu