kotun duniya ta tabbatar da hukumcin dauri rai da rai ga wasu tsofin shuwagabanin siyasar kasar 2
Kotun hukunta laifufukan yakin da aka yi a Rwanda mai samun goyan bayan kotun duniya, ta amince da hukuncin daurin rai da rai da aka yi wa wasu tsoffin shugabanin jam’iya mai mulkin kasar, da aka samu da laifin kisan kare dangin shekarar 1994.
Wallafawa ranar:
Mutanen biyu sun hada da Matthieu Ngirumpatse da Edouard Karemera, wadanda suka kasance shugaba da mataimakinsa na Jam’iyar National Revolutionary Movement for Development dake mulki lokacin kisan.
Wannan shara’a’ dai na cikin ta karshe da kotun zata yi, kafin kotun ta rufe kofarta a karshen wannan shekara ta 2014. Akalla mutane 800,000 aka kashe a rikicin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu