Isa ga babban shafi
Jamhuriyyar Congo

‘Yan Sanda sun bude wa masu zanga-zanga wuta a Congo

Rahotanni daga Jamhuriyar Congo na cewa ‘Yan sanda sun yi harbin bindiga a arangamar da suke yi da daliban Jami’a da ke zanga-zanga a birnin Kinshasa a yau Laraba. Akalla mutane 28 suka mutu tun fara kaddamar da zangar-zangar ta adawa da shirin gwamnati na sauya kundin tsarin mulki.

'Yan sandan Congo sun cafke wani daga cikin masu zanga-zanga a Kinshasa
'Yan sandan Congo sun cafke wani daga cikin masu zanga-zanga a Kinshasa AFP/Papy Mulongo
Talla

Wakilin Kamfanin Dillacin labaran Faransa ya ruwaito cewa ‘Yan sanda sun bude wa masu zanga-zanga wuta.

Sai dai Hukumomin kasar sun ce mutane biyar ne suka mutu a zanga-zangar ciki har da Dan Sanda guda da wasu daliban Jami’ar Kinshasa biyu lokacin da bangarorin biyu suka yi arangama.

A ranar Litinin ne mutanen Congo suka kaddamar da zanga-zangar adawa da shirin gwamnati na sauya kundin tsarin mulki domin ba Joseph Kabila damar ci gaba da shugabanci a kasar.

Matasa sun yi kone wasu gine ginen gwamnati a Kinshasa, yayin da fursunoni da dama suka tsere a gidan yari.

‘Yan adawa yanzu sun kira wani gagarumin gangami domin neman shugaba Kabila ya yi murabus wanda ya kwashe shekaru 14 yana shugabanci a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.