Faransa za ta taimakawa kasar Mali inji Francois Hollande
Shugaban Faransa Francois Hollande ya jaddada goyon bayan kasar ga al’ummar kasar Mali, tare da alkawali ci gaba da taimaka wa kasar domin ficewa daga matsaloli bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin gwamnati da kuma ‘yan tawayen kasar.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwa da fadar Elysees dake birnin Paris ta fitar jim kadan bayan tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Mali Ibrahim Boubakar Keita, Hollande ya ce Faransar za ta ci gaba da taimaka wa kasar a bangaren tattalin arziki da kuma siyasa domin samun nasarar wannan sulhu.
Faransa na daga cikin kasashen da suka taimaka domin ceto kasar Mali daga durkushewa bayan da yan tawayen arewacin kasar suka karbe ikon wasu yankunan kasar.
Gwamnatin Mali ta bayana matukar gamsuwar ta a wanan tayi daga Shugaban kasar Faransa Francois Hollande.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu