Isa ga babban shafi
Masar

Akalla mutane 70 sun mutu a mutsayar wuta tsakanin Sojin Masar da ISIL

Akalla mutane 70 ne suka rasa rayukansu mafi yawa sojoji a wata musayar wuta tsakanin mayakan ISIL da dakarun Kasar Masar a yankin Sinai. 

Jami'an tsaro tsaye a inda aka kai hari
Jami'an tsaro tsaye a inda aka kai hari REUTERS/Mohamed Abd El Ghany
Talla

A safiyar yau laraba ne mayakan ISIL suka kaddamar da kazamin harin a yankin Sheikh Zuweid dake arewacin kasar kan dakrun sojoji da ‘yan Sanda.

Mayakan dai sun kutsa kai ne acikin yankin dauke da bama-bamai a motoci, a wani yanayi na ba za ta.

Rahotani sun ce wannan harin shine mafi muni da mayakan suka kai a Sinai, tare da amfani da gurneti wajen tarwatsa ofishin ‘yan sandan yankin, baya ga tarwatsa shingayan bincike ababban hawa 15, da kuma harba rokoki a cikin sinai.

Sai dai kuma tuni Sojojin Masar suka far musu ta sama wanda a yanzu haka sunyi nasara kashe 38 daga cikin Mayakan.

Wannan harin dai na zuwa ne kwanaki biyu, bayan kashe mai shigar da karar kasar Hisham Barakat a wani harin bam a birinin Al-Kahira.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.