Sudan ta kudu za ta hukunta Sojojin da ke yi wa Mata Fyade
Gwamnatin kasar Sudan ta Kudu ta ce, za ta hukunta duk Sojan da aka samu da hannu wajen yi wa Mata fyade, jinjirar kasar da ke fama da yakin Basasa, kamar yadda wani rahoton Majalisar dinkin duniya ya sanar.
Wallafawa ranar:
Ma su bincike na tawagar Majalisar Dinkin Duniya a kasar Sudan ta kudu sun bayyana gano aikata kazaman laifukan cin zarafin dan adam da sojojin gwamnatin kasar ta Sudan ta Kudu suka aikata a kasar.
Rahoton ya dogara ne kan bayanan da shaidu 115 da abin ya shafa suka bayar, da kuma shaidun da Majalisar Dinkin Duniya ta tattara daga yankunan da aka aikata wannan mummunan cin zarafin matan da kuma fararen hula a kasar da yaki ya daidaita.
A lokacin da ya ke tsokaci kan rahoton na Majalisar Dinkin Duniya kakakin rundunar Sojan Sudan ta kudu Philip Aguer ya ce, sun karanta rahoton sun kuma ga abin da ya kunsa, don haka sun dau niyar daukar matakan hukunta wadanda aka samu da cin zarafin Mata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu