Isa ga babban shafi
Najeriya

An cafke wanda ya jagoranci hare haren Jos da Zaria

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta sun cafke mutumin da ya kitsa munanan hare haren ta’addanci da aka kai a biranen Jos da Zaria wanda ya lakume rayukan mutane sama da 70.

Mutane sama da 30 suka jikkata a harin Zaria da aka kai a Jihar Kaduna
Mutane sama da 30 suka jikkata a harin Zaria da aka kai a Jihar Kaduna REUTERS
Talla

01:01

Kakakin Rundunar Sojin Najeriya Kanal Sani Usman

Bashir Ibrahim Idris

Kakakin rundunar Sojin Najeriya Kanal Sani Usman Kukasheka ya ce an cafke mutumin ne da wasu mukararbansa guda biyu a Dadin Kowa daga Gombe lokacin da suke kokarin tserewa.

“Sojojinmu sun yi nasarar damke wadanda suka kai hare hare ta’addanci da aka kai a Masallaci da wurin cin abinci a garin Jos da kuma harin da aka kai a Zaria” a cewar Kanal Sani.

Yanzu haka mutanen suna amsa tambayoyi a hannun Jami’an tsaro.

Kanal Sani ya yi kira tare da neman hadin kan al’ummar Najeriya wajen bayar da goyon baya da bayanai da sirri ga jami’an tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.