Boko Haram ta kai hari a Burutai, kauyen Kwamandan Sojin Najeriya
Rahotanni daga Jihar Borno na cewa Mayakan Boko Haram sun kaddamar da hari a garin Buratai, cibiyar sabon babban hafsan Sojin Najeriya, inda mayakan suka kona gidaje ciki har da na ‘yan uwan kwamandan Sojin kasar da ya sha alwashin murkushe mayakan da ke addabar arewacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Akalla mutane biyu suka mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata, kamar yadda wasu Mazauna garin na Buratai suka tabbatarwa Kamfanin dillacin labaran Reuters.
Majiyoyin sun ce an kai harin ne a ranar Talata, amma ko da aka kai harin Babban Hafsan Sojin kasar Janar Tukur Buratai baya cikin garin.
Janar Tukur Buratai dai shi ne sabon babban hafsan sojin Najeriya da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada, wanda ya sha alwashin murkushe ayyukan mayakan Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu