Isa ga babban shafi
Najeriya

Majalisar Dattijai ta dage ranar tantance shugabannin tsaron Najeriya

Majalisar dattawan Najeriya ta dage ranar da za ta soma aikin tantance sabbin shugabannin rundunonin tsaron kasar da shugaban Muhammadu Buhari ya nada, aikin da ya kamata majalisar ta fara a yau Alhamis amma sai zuwa ranar talata ta makon gobe.

Sabon Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Bukola Saraki
Sabon Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Bukola Saraki REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Shugaban Majalisar dattawan Bukola Saraki, da farko ya ce za su fara aikin tantancewar ne a yau, kafin daga bisani ya ce sai a ranar Talata mai zuwa.

Majiyoyi sun ce an dage zaman ne domin samun damar halartar bukuwan karrama tsohon babban kwamandan askarawan kasar Alex Badeh da za a yi a yau.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.