Za a sake bitar shari’ar Sojojin Najeriya da aka yanke wa hukunci
Rundunar tsaron Najeriya ta ce za a sake bitar wasu daga cikin shari’o’in da aka yi wa sojojin kasar da ake zargi da gudu daga fagen daga da kuma wadanda suka aikata laifufuka daban daban.
Wallafawa ranar:
A cewar mataikamin shugaban sashen yada labarai na rundunar sojan kasar Kanal Sani Usman Kukasheka za a sake nazarin shari’ ar da ake wa wasu sojin kasar bisa korafe korafen da rudunar Sojin ta samu.
Kukasheka ya shaidawa RFI Hausa cewa za a bi shari’o’in ne dalla dalla domin yanke hukuncin da ya dace.
Sai dai ya ce wannan ba mataki ba ne da zai sa a dawo da wasu Sojojin da aka kora ba illa za a sake yin nazarin zargin da ake masu da kuma hukuncin da aka yanke masu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu