Isa ga babban shafi
Cote d'Ivoire

FPI ta zabi Nguessam dan takararta a zaben shugabancin Ivory Coast

Jam’iyyar FPI, ta tsohon shugaban Cote D’ivoire Laurent Bagbo ta zabi Pascal Affi Nguessam a matsayin dan takarta a zaben shugabancin kasar da za a gudanar a ranar 25 ga watan oktoban wannan shekara.

Affi N'Guessan, lokacin taron jam'iyyar FPI, ranar 21 ga watan mayun 2015 a Abidjan.
Affi N'Guessan, lokacin taron jam'iyyar FPI, ranar 21 ga watan mayun 2015 a Abidjan. AFP PHOTO/ SIA KAMBOU
Talla

Wakilan jam’iyyar sama da dubu 4 ne suka halarci wani gagarumin taro a jiya asabar a garin Trecheville, inda suka zabi Nguessam wanda ke rike da mukamin shugabancin jam’iyyar na kasa.

N’Guessam ya bukaci magoya bayan tsohon shugaba Bagbo wanda ke tsare a hannun kotun duniya, da su jefa masa kuri’unsu a zaben mai zuwa, inda ya ce hakan na a matsayin nuna karamci ga tsohon shugaban.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.