Mutane sun mutu a rikicin Kasar Mali
Mutane da dama sun rasa rayukansu a Kasar Mali sakamakon fafatawar da akayi tsakanin ‘Yan Tawayen Abzinawa da da masu goyawa gwamnatin Kasar baya kamar yadda majiyoyin tsaro suka tabbata
Wallafawa ranar:
Majiyoyin sun ce frikicin ya barke ne a Agnefis dake da nisan kilomita 120 daga garin Kidal, abinda yayi sanadiyar mutuwar mutrane da dama.
Dakarun Majalisar Dinkin Duniya dake aikin samar da zaman lafiya a kasar sun bayyana fadan a matsayin karya yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a yan kwanakin da suka gabata.
Dkarun sun kara da cewa, kasashen duniya sun damu kan yadda ake ci gaba da karya yarjejeniyar ta zaman lafiya, lamarin dake barazana dangane da dauwawammiyar zaman lafiya a Kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu