Isa ga babban shafi
Kamaru

Boko Haram ta kashe mutane 9 a Kolofata cikin Kamaru

Akalla mutane 9 suka mutu yayin sama da 20 suka jikkata a wasu hare haren kunar bakin wake guda biyu da aka kai a garin Kolofata arewacin Kamaru a ranar Lahadi.

Mayakan Boko Haram sun kashe mutane da dama a arewacin Kamaru
Mayakan Boko Haram sun kashe mutane da dama a arewacin Kamaru Journal du Cameroun / David Wanedam
Talla

Ana kyautata zaton Mayakan Boko Haram ne suka tayar da bama baman.

‘Yan kunar bakin waken sun tayar da bama baman ne da ke jikinsu a lokacin da ‘Yan banga suka tunkare su bayan sun nufi kasuwa.

Wada Alhaji wani Dan jarida a Kamaru ya shaidawa RFI Hausa cewa ‘Yan banga da aka daura wa alhakin tsaro a Kolafata ne suka gano ‘Yan kunar bakin waken guda biyu daure da bama bamai a jikinsu

A cewarsa sun tayar da bama baman ne a lokacin da aka nemi a kama su.

Garin Kolafata dai na kan iyaka ne da yankin arewa maso gabashin Najeriya mai fama da Boko Haram, kuma an dade mayakan na kai hare hare a garin.

Kasar Kamaru  na cikin rundunar kawance 5 da suka hada da Najeriya da Chadi da Nijar da Benin da ke tunkarar mayakan Boko Haram.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.