Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Diendere ya bukaci Sojoji su mika wuya

Shugaban Sojin da ya jagoranci juyin mulkin kasar Burkina Faso Janar Gilbert Diendere ya sanar da cewar an kawo karshen harin da sojojin da ke yiwa gwamnatin kasar biyaya suka kai kan dakarun sa a barikin su da ke Ouagadougou.

Janar Gilbert Diendéré
Janar Gilbert Diendéré REUTERS/Joe Penney
Talla

Wata sanarwa da jagoran juyin mulki Janar Gilbert Diendere ya yi, ya bukaci magoya bayan sa da su aje makaman su dan kaucewa zub da jinni a ciokin kasar.

Rahotanni sun ce anji karar fashewar manyan makami a barikin sojojin dake gadin fadar shugaban kasar, sakamakon kawanyar da sojojin dake biyaya ga gwamnatin farar hula suka musu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.