Bakonmu a Yau
Majalisar dokokin Nijar ta amince da kasafin kudin kasa na 2016
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:46
A yau laraba Majalisar Dokokin Jamhuriyar Nijar ta jefa kuri’ar amincewa da kasafin kudin kasar na shaekara mai zuwa da gagarumin rinjaye, kasafin da ya tashi sama da cfa bilyan dubu daya da bilyan dari bakwai da tamanin da shida.Honnorable Zakari Oumarou, shugaban masu rinjaye a zauren majalisar ya yi wa Abdoulkarim Ibrahim Sahikal Karin bayani kan dalilansu na amincewa da kasafin.