Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari ya karrama Golden Eaglets da suka lashe kofi a China a 1985

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karrama ‘yan wasa da dama a birnin Abuja tun daga bangaren kwallon kafa zuwa kwallon Kwando da damben zamani zuwa ‘yan wasan daga nauyi da dara.

Bayan shekaru 30 Shugaban Najeriya ya cika alkawalin da ya dauka na karrama 'Yan wasan Golden Eaglets da suka lashe kofi a China
Bayan shekaru 30 Shugaban Najeriya ya cika alkawalin da ya dauka na karrama 'Yan wasan Golden Eaglets da suka lashe kofi a China Dalung via facebook
Talla

Cikin wadanda aka karrama da kudi sun hada da ‘Yan wasan da suka lashewa Najeriya kofi na ‘yan kasa da shekaru 17 na farko wadanda shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi wa alkawali tun shekaru 30 da lashe kofin duniya a China.

Shugaban ya bai wa kowanne daga cikin ‘Yan wasan Naira Miliyan biyu.

‘Yan wasan dai sun lashe kofin ne a 1985 a lokacin da buhari na shugaban kasa a mulkin soja. Amma bai cika alkawalin ba saboda juyin mulkin da aka yi ma shi

Akwai wadanda suka mutu, amma daya daga cikinsu Sani Adamu ya bayyanawa RFI Hausa farin cikinsa.

“Tunawa da mu ya faranta min rai, hakan ya nuna ba a manta da mu ba”, a cewar Adamu wanda suka lashe wa Najeriya kofi a China.

Shugaba Buhari ya ce ya godewa Allah da ya sa yana raye domin samun damar cika alkawalin.

Matasa ma da suka lashe kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 17 a shekarar da ta gabata sun karbi kudi Naira miliyan guda da dubu dari biyu, yayin da aka ba mai horar da su Emmanuel Amuneke dubu dari tara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.