Isa ga babban shafi
Boko Haram

Sojoji sun kashe 'yan Boko Haram 92 a Kumshe

Gwamnatin Kamaru ta bayyana cewa, Rundunar sojinta ta kashe mayakan Boko Haram 92 tare da ceto mutane 850 daga hannunsu a wani samamen hadin gwiwa da sojojin Najeriya.

Sojojin Kamaru sun kashe mayakan Boko Haram 92 a wani samamen hadin gwiwa da Najeriya
Sojojin Kamaru sun kashe mayakan Boko Haram 92 a wani samamen hadin gwiwa da Najeriya Reuters
Talla

Wata sanarwa da ministan yada labaran Kamaru, Issa Tchiroma Bakary ya fitar ta ce, dakarun sun kai samamen ne a kauyen Kumshe na jihar Borno da ke kan iyakar kasashen biyu.

Ministan ya ce, sojojin Kamaru guda biyu sun rasa rayukansu yayin da biyar suka jikkata a samamen bayan wata nakiya ta tashi cikin kuskure.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.