Isa ga babban shafi
Sudan ta kudu

Riek Machar zai koma birnin Juba

Madugun ‘yan tawaye kuma tsohon mataimakin shugaban Sudan ta Kudu Riek Machar ya ce zai koma birnin Juba a ranar 18 ga wannan wata, karo na farko bayan fice warsa daga birnin a watan disambar shekara ta 2013.

Madugun 'yan tawayen Sudan ta kudu Riek Machar
Madugun 'yan tawayen Sudan ta kudu Riek Machar SAAC KASAMANI / AFP
Talla

Bayan ya isa a Juba ne za a yi bikin kafa sabuwar majalisar ministoci ta gwamnatin rikon kwarya tsakanin Riek Machar da kuma Salva Kiir.

Sama da mutane 150,000 ne suka tserewa gidajensu a rikicin Sudan ta kudu da ya tursasawa sama da mutane miliyan biyu gudun hijira.

A na sa rai dai dawowar Machar tare da kafa gwamnatin hadaka zai kawo karshan zub da jini da tashin hankalin da kasar ta tsinci kanta a ciki shekara biyu bayan balewar daga Sudan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.