Isa ga babban shafi
Libya

Kasashen Duniya 50 Na Taro Don Taimakawa Libya

Wakilan kasashen duniya 50 na wani taro a birnin Tunis na kasar Tunisiya domin muhawara gameda irin gudunmawar da za su bayar domin karfafa wa Gwamnatin hadin kai na kasar Libya.

Shugaban riko na Gwamnatin hadaka na Libya  Fayez el-Sarraj
Shugaban riko na Gwamnatin hadaka na Libya Fayez el-Sarraj AFP PHOTO / FETHI BELAID
Talla

Taron na kwana daya ya kasance Majalisar Dunkin Duniya da kuma kasar Britaniya suka shirya da niyyar ganin an baiwa Gwamnatin hadin kan kasar Libya damar warware tsarin ta na sake gina kasar bayar yaki na tsawon shekaru biyar.

Fayez al-Sarraj, shugaban Gwamnatin Hadakan ya isa birnin Tripoli ta jirgin ruwa, makonni biyu da suka gabata, tare da rakiyar Dakaru na musamman da suka kunshi sojan ruwa, kuma har ya sami amincewar wasu Hukumomin kasar.

Wakilan kasashe 40 suka halarci zaman taron na Talata a Tunis sai kuma kungiyoyi daban-daban na duniya.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.