Isa ga babban shafi
Nijar

Kungiyar Alkalan Nijar ta soki Issoufou

Kungiyar alkalai SAMAN a Jamhuriyar Nijar ta zargi shugaban kasar Issoufou Mahamadou da kokarin tauye ‘yancin da kundin tsarin mulkin kasar ya bai wa bangaren shari’a, saboda yadda shugaban ke canzawa alkalai wuraren aiki ba tare da an bi ka’ida ba.

Shugaba Mohammadu Issoufou, na Nijar
Shugaba Mohammadu Issoufou, na Nijar ISSOUF SANOGO / AFP
Talla

A zantawarsa da RFI Hausa, Mataimakin shugaban kungiyar alkalan Nouhou Boubakar,  ya ce Shugaba Issoufou na nada wadanda ya ke da alakar siyasa da su ba tare da la’akari da kwarewar aikin shari’a ba.

Kungiyar Alkalan ta soki  Issoufou ne kan nada wani Dan Jam’iyyarsa ta PNDS Tarayya a matsayin alkalin wata babbar Kotun da ke kula da dukiyar kasa wato Cour des Comptes.

Alakalan na ganin nada dan siyasa mataki ne da zai janyo rikici da tabbatar da rashin adalci ga aikin tafiyar da babbar kotun.

Sannan Kungiyar ta ce kundin tsarin mulkin Nijar ya haramta hada siyasa da ‘yancin aikin Shari’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.