Isa ga babban shafi
Najeriya

An dawo da dokar hana fita a wasu yankunan Kaduna

Gwamantin Jihar Kaduna ta dawo da dokar hana fita a kananan hukumomin da ke fama da rikici a kudancin jihar bayan sassauta dokar saboda bukukuwan Kirsimeti.

Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i
Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i facebook
Talla

An dai sassauta dokar daga sa’o’I 24 zuwa 12 domin bai wa jama’a damar gudanar da bukukuwan kirismeti a cikin sauki. Amma dokar za ta ci gaba da aiki sakamakon hare-hare da ake fuskanta a yankunan.

Samuel Aruwan da ke magana da yawun gwamnan Jihar ya shaidawa RFI Hausa cewa daga yau Talata dokar za ta koma ta tsawon sa’o’I 24 a kananan hukumomin jihar guda uku wato Jema’a da Kaura da kuma Kataf.

An samu salwantar rayuka sakamakon rikici tsakanin makiyaya da wasu kabilun yankin na kudancin kaduna.

03:09

Rahoton Aminu Sani Sadu daga Kaduna

RFI

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.