Nijar
An tsawaita wa'adin kula da lafiyar Mata a asibitocin Nijar
Ma’aikatar kiwon lafiya a Jamhuriyar Nijar sun tsawaita wa’adin aikin kula da mata da kananan yara a cikin asibitocin kasar, musamman matan da ke da juna biyu da kuma wadanda ke zuwa asibiti domin duba yara kanana. A can baya dai ana gudanar da aikin ne tsakanin karfe 8 zuwa karfe 11 na safiya, to sai dai lura da yadda mata ke fuskantar matsaloli a duk lokacin da suke je asibiti, wannan ya sa aka tsawaita wa’adin har zuwa karfe biyar na marece. Wakilinmu a Maradi Salisu Issa ya aiko da rahoto.
Wallafawa ranar:
Talla
An tsawaita aikin kula da lafiyar Mata a asibitocin Nijar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu