Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram : Mata sun fara kai hari da goyo

Hukumar agajin gaggawa a Najeriya NEMA, ta ce wata mata da ta kai harin kunar bakin wake a Madagali da ke cikin Jihar Adamawa a arewacin kasar tana dauke ne da goyo a lokacin da ta kai harin.

Taswirar  Madagali a yankin Jihar Adamawa
Taswirar Madagali a yankin Jihar Adamawa
Talla

Jagoran Hukumar NEMA a Jihar Adamawa Saad Bello wanda ya tabbatar da Matar na dauke da goyo a lokacin da ta kai harin a Madagali, ya ce ga alama wannan wani sabon salo ne da kungiyar Boko Haram ta fara amfani da shi domin kai hare-harenta.

Akalla mutane biyu suka mutu sannan 15 suka jikkata a harin wanda aka kai a wani shingen binciken sojoji da ke kusa da tashar shiga mota a Madagali a ranar 13 ga Janairu.

Boko Haram dai ta dade tana amfani da Mata da Kananan yara a hare haren kunar bakin waken da ta ke kai wa a makarantu da kasuwa da wuraren ibada da kuma jami'an tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.