An kai hari Jami’ar Maiduguri
Wasu ‘Yan kunar bakin wake sun kai hare haren bama bamai a ciki da wajen Jami’ar Maiduguri, inda rahotanni suka ce daya daga cikin jami’an Jami’ar ya mutu sannan kuma biyu sun samu raunuka.
Wallafawa ranar:
Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta ce wasu ‘yan kunar bakin wake uku ne suka kai hari kan jami’an tsaron da ke jami’ar Maiduguri a cikin daren jiya Lahadi da ake bikin Sallah.
Maharan wadanda mata ne dukkaninsu sun mutu, inda daya ta tayar da bom din a cikin Jami’ar, daya kuma jami’an tsaro suka harbe ta a lokacin da ta ke kokarin shiga jami’ar.
Mai maigana da yawun rundunar ‘yan sanda a Jihar ta Borno DSP Victor Isuku da ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an tayar wani bom wata unguwa da ke birnin Maiduguri a ranar Sallah.
‘Yan Boko Haram dai sun sha kai hare hare a Jami’ar Maiduguri.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu