Isa ga babban shafi
Rwanda

Shugaba Paul Kagame Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Rwanda

Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame ya lashe zaben shugabancin kasar inda zai fara wa'adi na uku bayan alkaluman sakamakon zaben na nuna ya sami yawan kuri'u kashi 98% na yawan kuri'u da aka jefa.

Shugaba  Paul Kagame cikin wani hoto a shekara ta 2000.
Shugaba Paul Kagame cikin wani hoto a shekara ta 2000. rfi.
Talla

Kashi 80% na yawan kuriun ne dai aka kirga ya zuwa yammacin jiya Asabar kamar yadda Hukumar zaben kasar ta sanar.

A cewar Hukumar zaben Kashi 97% na jimillan masu jefa kuri'u kusan miliyan bakwai  suka jefa kuri'a as yayi zaben na Lahadi.

Shugaban Hukumar Zaben Kalisa Mbanda ya gaskata cewa Shugaban kasar Paul Kagame yayi gagarumin nasarar lashe zaben.

Paul Kagame mai shekaru 59  ya kwashe shekaru 17 yana mulkin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.