Isa ga babban shafi
Chadi

Cutar amai da gudawa ta kashe mutane 52 a Chadi

Hukumomin kiwon lafiya a kasar Chadi sun sanar da barkewar cutar amai da gudawa wadda tuni ta lakume rayukar mutane 52, bayan ta kama mutane 312.

Shugaban Chadi Idris Deby Itno
Shugaban Chadi Idris Deby Itno REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

Sakataren ma’aikatar lafiyar kasar Hamid Djabar, ya ce tuni suka kafa kwamitin gaggawa wanda zai yi aikin dakile yaduwar cutar, tare da aiki da hukumar UNICEF da kuma jami’an kungiyar agaiji ta Medicins Sans Frontiers.

 

A shekarar 2011 an samu barkewar irin wannan cutar, mutane 17,200 suka kamu, yayin da sama da 450 suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.