Isa ga babban shafi

'Yansanda sun tarwatsa 'yan Shi'a masu zanga-zanga a Abuja

Jami'an 'Yansanda a Abuja babban birnin Najeriya sun tarwatsa wani dandazon mabiya Shi'a da suka shirya zanga-zangar adawa da ci gaba da rike jagoransu Sheikh Ibrahim Zakzaky da gwamnatin kasar ke ci gaba da yi tsawon lokaci.

Jagoran mabiya mazhabar Shi'a a Najeriya El-Zakzaky
Jagoran mabiya mazhabar Shi'a a Najeriya El-Zakzaky REUTERS
Talla

Wannan dai ba shi ne karon farko da Mabiya na Shi'a ke gudanar da makamanciyar zanga-zangar ba, inda a lokuta da dama jami'an tsaro kan tarwatsa su.

Mabiyan dai na bukatar lallai gwamnatin Najeriyar karkashin shugaba Muhammadu Buhari ta mutunta umarnin kotu wajen sakin Jagoran na su Ibrahim Yakubu Zakzaky da ta ke rike da shi kusan shekaru biyu.

Jami'an tsaron sun yi amfani da hayaki mai sanya hawaye kan dandazon mabiyan na Shi'a don tarwatsa su.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.