Isa ga babban shafi
Rwanda-Faransa

Paul Kagame ya gana da Emmanuel Macron

Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame ya gana da Shugaban Kasar Faransa Emmanuel Macron a fadar Elysee, a kokarin sun na bunkasa hulda tsakanin kasashen biyu, bayan shekaru 20 na zanga zangar kisan kare dangi a Rwanda da gwamnatin Rwanda ta zargi Faransa da taimakawa wajen kisan yan kasar ta.

Paul Kagame na Rwanda da Shugaban Faransa Emmanuel Macron a fadar Elysee
Paul Kagame na Rwanda da Shugaban Faransa Emmanuel Macron a fadar Elysee LUDOVIC MARIN / AFP
Talla

Shugaban kasar Rwanda dake ci gaba da fuskantar suka daga wasu yan kasar ,ya bayyana fatan sa na samu goyan bayan Faransa ga takarar Ministan Rwanda a kujerar Shugabancin kungiyar dake amfani da harshen Faransanci.

Paul Kagame yayi amfani da wannan dama domin ganawa da wasu Shugabanin kamfanonin sadarwa na Facebook a lokacin cin abinci bisa gayatar Shugaban Faransa, Rwanda na daga cikin kasashen Afrika da suka samu ci gaba na musaman ta fuskar ingata sashen sadarwa na intanet.

A ganawa da Shugaban kasar ta Rwanda Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana cewa zai halarci taron kungiyar Africa a Mauritania, taron da zai gudana a watan Mayu na wannan shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.