Afrika ta kudu da kujerar memba a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya
A jiya juma’a ne aka zabi kasashen Jamus, Belgium, Afrika ta Kudu, Indonesia da jamhuriyar Dominicaine a matsayin memba ba na dindin ba a kwamity tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.
Wallafawa ranar:
Wakilan kasashen za su soma aiki kama daga watan Janairu shekara 2019 zuwa 2021.
Jamus ta samu goyan bayan kasashe 184, Belgium 181, Afrika ta kudu 183, Indonesia 144 sai Jamhuriyar Dominicaine shine karo na farko da kasar ta shiga sahun wakilai a wannan kujera ta samu kuri’u 184.
Kwamity tsaro na Majalisar Dinkin Duniya na da membobi 15, biyar daga cikin su na da matsayin memba dake da kujeru na dindin da suka hada da Amurka, Rasha, China, Faransa, Ingila.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu