Isa ga babban shafi
Nijar-Boko Haram

Sojin Nijar sun hallaka mayakan Boko Haram 33 a Diffa

Ma'aikatar tsaron Jamhuriyyar Nijar ta ce sojinta sun yi nasarar hallaka mayakan Boko Haram 33 a wani sumame da suka kai maboyar mayakan da ke yankin kudu maso gabashin kasar da ke yankin tafkin Chadi.

Ma'aikatar Nijar ta ce bayan fatattakar mayakan ta kuma yi nasarar kwace tarin makamai daga maboyar ta 'yan boko Haram
Ma'aikatar Nijar ta ce bayan fatattakar mayakan ta kuma yi nasarar kwace tarin makamai daga maboyar ta 'yan boko Haram AFP PHOTO/HO/NIGERIAN ARMY
Talla

Ma'aikatar tsaron ta Nijar ta kuma tabbatar da kame tarin makamai da motoci daga hannun mayakan na Boko Haram, inda ta ce babu ko sojanta guda daya rasa ransa a sumamen na jiya Talata.

Cikin kayakin yakin da sojinta suka kame a cewar ma'aikatar tsaron, har motoci masu sulke wadanda sanarwar ta ce tuni sojinta suka lalata su, sai kuma babura 2 da bindigogi kirar AK47 10 da kuma makamai masu linzami baya ga harsasai kusan dubu 4 da sauran muggan makamai.

Sumamen dakarun sojin na Nijar ya zo ne bayan kisan jami'an 'yan sanda 7 a wani hari da ya kai ga kisan mayakan jihadi 38 a jihar Diffa wadda ke fama da hare-haren Boko Haram.

Kawo yanzu dai akalla mutane dubu 27 aka yi ittifakin sun mutu a jihar ta Diffa tun bayan farowar rikicin Boko Haram a shekarar 2009, kari akan 'yan mata kusan 20 da mayakan suka yi garkuwa da su cikin watan Nuwamba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.