Afrika
An sake kashe wani dan Najeriya a Afrika ta kudu
Kungiyar yan Najeriya mazauna Afrika ta kudu tace an sake kashe wani dan kasar Tony Elechukwu, lokacin da wani dan bindiga ya dirka masa harsashi a yankin Witbank Mpumalanga.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban yan Najeriya mazauna kasar, Ben Okoli ya tabbatar da aukuwar lamarin a wasikar da ya aikewa ofishin Jakadancin Najeriya a Johannesburg.
Okoli yace wannan shine karo na uku da ake kashe yan najeriya a cikin wannan wata, bayan wadanda aka kashe a ranakun 6 ga wata da 9 ga wata.
Jakadan Najeriya Godwin Adama yayi Allah wadai da kisan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu