'Yan bindiga sama da 100 sun kai hari Madarounfa
'Yan bindiga da aka bayyana cewa adadinsu ya fi dari daya sun kai kari a wani gari mai suna Shirge dake yankin Madarumfa a jihar Maradin Jamhuriyar Nijar a cikin daren jiya alhamis.
Wallafawa ranar:
Gwamnan jihar Zakari Oumarou ya tabbatar da mutuwar mutane akalla 5 a wannan hari, inda ya ce har zuwa safiyar yau ana cigaba da fafatawa tsakanin 'yan bindigar da kuma jami'an tsaron kasar ta Nijar.
Madarumfa yanki ne da yayi iyaka da jihohin Katsina da Zamfarar tarayyar Nigeria mai fama da 'yan bindiga.
Rahotanni daga rundunnar tsaron Nijar na bayyana cewa tuni aka aiko da jirgin saman yaki don taimakawa dakarun dake kasa, wannan yankin ya kasance wani yankin da ake satar mutane don neman kudin fansa .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu