Isa ga babban shafi
Najeriya-MDD

Shekaru 8 bayan harin Boko Haram MDD ta bude Ofishinta a Abuja

Majalisar Dinkin Duniya ta sake bude Ofishinta da ke Abuja babban birnin Tarayyar Najeriya bayan kulle shi fiye da shekaru 8 sanadiyyar wani harin kunar bakin wake a Ofishin wanda ya kai ga daukar matakin kulle shi.

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya bayan harin ta'addancin shekaru 8 da suka gabata.
Ofishin Majalisar Dinkin Duniya bayan harin ta'addancin shekaru 8 da suka gabata. REUTERS/NTA via
Talla

Harin wanda kungiyar Boko Haram ta kaddamar a Ofishin na Majalisar Dinkin Duniya ya hallaka mutane 23 nan take baya ga jikkata wasu da dama.

A tsawon shekaru 8 da suka gabata, Majalisar Dinkin Duniyar na amfani da wasu kananun gine-ginenta ne don ci gaba da harkokinta.

Cikin sanarwar da Ofishin Majalisar ya fitar ya nuna cewa yanzu haka jami’an Ofishin sun koma ayyukansu gadan-gadan a tsohon Ofishin na su mai hawa 4 a tsakiyar birnin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.