Isa ga babban shafi
Algeria

'Yan Algeria na bikin tuna farkon zanga-zangar hambarar da Bouteflika

Dubun dubatar mutane ne suka yi tururuwa zuwa gangamin cika shekara guda da zanga zangar da ta haifar da kawar da gwamnatin shugaba Abdelaziz Bouteflika na Algeria a birnin Algiers.

Wasu masu zanga-zangar Algeria.
Wasu masu zanga-zangar Algeria. (Reuters/Ramzi Boudina)
Talla

Masu zanga zangar sun yi ta nuna adawar su da mulkin soji da kuma bukatar kafa gwamnatin farar hula a kasar wadda ta samu ‘yancin kai daga Faransa a shekarar 1962.

Ita dai zanga zangar ta barke ne ranar 22 ga watan Janairu lokacin da tsohon shugaban kasa Abdelaziz Bouteflika ya bayyana aniyar sa ta yin sabuwar takara domin yin wa’adi na biyar duk da tsananin rashin lafiyar da yake fama da ita.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.