Isa ga babban shafi
Sahel

Kasashen Sahel sun sha alwashin cigaba da barin wuta kan 'yan ta'adda

Taron kasashen dake rundunar G5 Sahel da aka yi a Mauritania ya amince da shirin ci gaba da budewa ‘yan bindiga wuta, wadanda hare-haren da suke kaiwa a cikin kasashe guda 3 na yankin yayi sanadiyar salwantar dubban rayuka da kuma karya tattalin arzikinsu.

Wani sojin Faransa tare da dakarun rundunar G5 Sahel.
Wani sojin Faransa tare da dakarun rundunar G5 Sahel. AFP Photo/MICHELE CATTANI
Talla

A lokacin da yake tsokaci a zaman taron da ya samu halartar kasashen Burkina Faso, Mali, Jamhuriyar Nijar da kuma Chadi, shugaban Mauritania mai masaukin baki Mohamed Ould Cheikh El Ghazouani, ya ce kasashen na bukatar hadin kai da kasashen duniya wajen kawo karshen tashe tashen hankulan da yankin na Sahel ke fuskanta.

Tun a shekarar 2014 kasashen na Sahel ke gudanar da aikin hadin guiwa domin tabbatar da tsaro a yankin sakamakon yadda suke fama da mayakan kungiyoyin ta’addanci alámarin da ya haifar da mummunan koma bayan ci gaban alúmma, tsaro da kuma muhalli.

A shekarun baya bayan nan ne dai tashe-tashen hankulan dake addabar yankin arewacin Mali, suka yadu zuwa tsakiyar kasar, da kuma kasashen Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.

Wata kididdiga da majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ta nuna cewar hare-haren ‘yan ta’adda da rikicin kabilanci, sun yi sanadin mutuwar kimanin mutane dubu 4, adadin da ya rubanya har sau 5 idan aka kwatanta da shekarar 2016, duk kuwa da kasancewar dakarun wanzar da zaman lafiyar kasashen Afrika, na majalisar ta dinkin duniya da kuma na Faransa a Yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.