Isa ga babban shafi
Afrika

An sace jagoran yan Adawa na Mali

Gwamnatin Mali ta tabbatar da sace Shugaban babban jam’iyyar adawar kasar Soumaila Cisse, irinsa na farko da aka taba yi wa wani babban dan siyasa a kasar dake yammacin Afrika da ke fama da yaki da kungiyoyin yan ta’adda dake ikirarin jihadin musulunci.

Soumaila Cisse,Shugaban yan adawar kasar Mali
Soumaila Cisse,Shugaban yan adawar kasar Mali MICHELE CATTANI / AFP
Talla

An sace shugaban yan adawar kasar Mali Soumaïla Cissé ne a lokacin da yake tsakiyar yakin neman zaben yan majalisar dokoki da ake shirin gudanarwa a ranar lahadi 29 ga wannan watan da muke cikin sa.

Soumaïla Cissé, mai shekaru 70 da haihuwa a duniya wanda sau uku jere ga juna yana neman mukamin shugabancin kasar, a ranar larabar da ta gabata ne wata tawagar mutane sama da 12 dake cikin mota kirar Hilux suka sace shi a mazabarsa ta Niafounké, dake cikin yankin Tombouctou. Bayan da suka kashe mai tsaron lafiyarsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.