Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

'Yan bindigar ADF sun kashe fararen hula 25 a Jamhuriyar Congo

Akalla mutane 25 sun mutu a wani hari kan al’ummar yankin Beni na Arewacin Kivu a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo, farmakin da mahukuntan kasar suka dora alhakinsa kan ‘yan bindigar kungiyar ADF da suka yi kaurin suna wajen kisan fararen hula a shekarun baya-bayan nan.

Wasu Sojin Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo a yakin da su ke da 'yan bindigar ADF a yankin arewacin Kivu.
Wasu Sojin Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo a yakin da su ke da 'yan bindigar ADF a yankin arewacin Kivu. Reuters
Talla

Babban jami’in da ke kula da yankin na Beni Donat Kibuana ya ce an gano gawarwakin mutanen 25 ne lokacin da Soji ke bin sahun wasu mayakan ADF zuwa maboyarsu a daren jiya Alhamis.

A cewar jami’in, lamarin ya faru ne a kauyen Tingwe mai tazarar mil biyar da kauyen Eringeti yankunan da mayakan na ADF ke yawaita kai farmaki tare da hallaka tarin fararen hula.

Sai dai shugaban kungiyoyin fararen hula a yankin na Tingwe, Bravo Mohindo Vukulu ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa adadin mutanen da suka mutu a farmakin ka iya zarce 30 la’akari da yadda ake ci gaba da laluben wasu gawarwakin.

Mr Vukulo ya ce mutanen su na tsaka da shirye-shiryen bikin sabuwar shekara ne ‘yan bindigar na ADF suka yi musu dauki dai-dai tare da yi musu kisan gilla, wanda zuwa yanzu ba a kammala gano adadinsu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.