Isa ga babban shafi
Afrika

Zan kawo gyara ta fuskar tsaro- Buhari

Matsallar cin zarafin da ake zargin jami’an tsaron Najeriya na ci gaba da ciwa shugaban Najeriya tuwo a kwariya, Shugaba  Muhammadu Buhari  ya dau alkawali kawo gyara inda yake cewa masu zanga-zangar EndSARS da ta fi muni a jihar Lagas na dada nuni irin matsaloli da jama’a ke fuskanta,ya zama wajibi gwamnatin sa ta saurari koken mutan kasar ta fuskar tsaro da kuma kare hakkokin jama’a.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. Nigeria Presidency/Handout / REUTERS
Talla

Shugaba Buhari na magana ne a yayin da yake gabatar da jawabin sabuwar shekara gay an kasar kamar yada jaridar Premium Times dake Njaeriya ta ruwaito.

Ya zuwa yanzu kungiyoyi daga ciki da wajen kasar sun zura idanu suna dakon sakamakon binciken da sama da jihohi 20 na kasar suka kaddamar biyo bayan zargin da ake yiwa jami’an tsaro na azabatar da farraren hula a Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.