Isa ga babban shafi
Afrika

Fada ya barke tsakanin yan Sanda da mazaunan Dakar

‘Yan sandan Senegal sun yi arrangama da wani gungu daga cikin daruruwan matasan da suka fantsama kan titunan yankin Ngor dake birnin dakar inda suke zanga-zangar adawa da matakan takaita walwalar da gwamnati ta kafa don dakile yaduwar annobar coronavirus ciki har da hana fitar dare.

Wasu daga cikin manyan titunan birnin Dakar na kasar Senegal
Wasu daga cikin manyan titunan birnin Dakar na kasar Senegal RFI/Manon Laplace
Talla

Matasan sun yi ta kona tayoyi gami da kafa shingayen hana zirga-zirga a kan tituna yayin boren abinda ya sanya ‘yan sanda amfani da karfi wajen kokarin tarwatsa su.

Ranar laraba  shugaban Senegal Macky sall ya ayyana dokar ta baci a wasu yankunan kasar ciki har da birnin Dakar, inda ya kafa dokar hana fitar dare daga karfe 9 zuwa 5 na safiya, don dakile yaduwar annobar Korona.

Wasu kasashen na Afrika na dab da yi koyi da kasar ta Senegal a wannan shiri na takaita zirga-zirgar jama'a sabili da cutar Coronavirus dake ci gaba da lakume rayukan jama'a a Duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.