Isa ga babban shafi
DR Congo

Shugaba Tshisekedi ya nada sabon Firaministan DR Congo

Shugaban Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo Felix Tshisekedi ya nada Jean-Michel Sama Lukonde Kyenge a matsayin Firaminista bayan kwahse dogon lokaci ana fama da rikicin siyasa a kasar.

Shugaban kasar Congo Félix Tshisekedi.
Shugaban kasar Congo Félix Tshisekedi. Sumy Sadurni / AFP
Talla

Sama Lukonde mai shekaru 43 zai maye gurbin Sylvester Ilunga Ilunkamba wanda aka tilastawa barin mukamin sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Tshisekedi da Joseph Kabila.

Kabila da ya taimakawa Tshisekedi hawa karagar mulki kuma suka kafa gwamnatin hadin kai, yanzu haka basa ga maciji da juna a tsakanin su, yayinda Tshisekedi ke gaba da kakkabe mukarraban Kabila daga cikin gwamnatin.

A ranar 29 ga watan Janairu ne Firaminista Sylvester Ilunga Ilunkamba ya yi murabus bayan kada masa kuri’ar yankan kaunar da yan majalisun kasar suka yi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.