Isa ga babban shafi
DR Congo

An kashe sama da mutane dubu 2 a Congo-MDD

Sama da fararen hula dubu 2 suka rasa rayukansu a larduna uku na Jamhuriyar Demokuradiyar Congo a shekarar 2020 sakamakon hare-haren ‘yan bindiga kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana, tana mai nuna damuwa kan yadda matsalar ke dada kamari.

Sojojin Majalisar Dinkin Duniya da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Congo
Sojojin Majalisar Dinkin Duniya da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Congo MONUSCO/Force
Talla

Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce, wuraren da aka tanadar wa mutanen da suka rasa muhallansu a arewacin Kivu na ci gaba da fuskantar hare-hare yanzu haka.

Sama da 'yan gudun hijira dubu 88 ke rayuwa a sansanoni 22 da Majalisar Dinkin Duniya ta samar musu bayan rasa muhallansu a arewacin Kivu.

Rahotanni sun ce, kungiyoyin 'yan bindigan sun mamaye makarantu da gidajen al'umma, yayin da suke kaddamar da farmaki kan cibiyoyin kula da lafiya.

Sama da mutane miliyan 5 rikici ya raba da gidajensu a Jamhuriyar Demokuradiyar Congo cikin shekaru biyu da suka gabata, inda kididdiga ta nuna cewa, a arewacin Kivu kawai, mutane miliyan biyu aka kora daga gidajensu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.